Shugaba Tinubu Ya Yi Naɗin Farko Da Adeleke, Da Sauransu

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya nada Ambasada Kunle Adeleke a matsayin shugaban ka’ida na kansa ( Chief Protocol) (SCOP) ga shugaban kasa.

Rahotannin da ba a tabbatar da su ba sun nuna cewa an nada Mista Dele Alake wanda ya dade a kan Mista Tinubu da Olusegun Dada jagoran matasa a matsayin mai magana da yawunsa da kuma mai taimaka wa shugaban kasa kan kafafen yada labarai na zamani.

A halin da ake ciki, PRNigeria ta tattaro cewa za a fitar da cikakken jerin sunayen masu taimaka wa shugaban kasa da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima a hukumance ranar Talata.

Daga PRNigeria

Nan ba da jimawa ba za a sanar da sauran nadin mataimakan

By:

Posted in:


Leave a comment

Design a site like this with WordPress.com
Get started