Da duminsa: Tinubu ya nada Gbajabiamila a matsayin shugaban ma’aikata, Akume a matsayin SGF

Shugaban ya kuma nada Goerge Akume a matsayin sakataren gwamnatin tarayya.

By… Huzaif Usman



Yuni 2, 2023

Shugaba Bola Tinubu ya nada kakakin majalisar wakilai Femi Gbajabiamila a matsayin shugaban ma’aikatan fadar sa.

Shugaban ya kuma nada George Akume Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF).

Mista Akume, tsohon gwamnan jihar Benue, shi ne tsohon ministan ayyuka na musamman a gwamnatin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Hakazalika, Mista Tinubu, a wata sanarwa a ranar Juma’a mai dauke da sa hannun Abiodun Oladunjoye, daraktan yada labarai a fadar gwamnati, ya bayyana Ibrahim Hassan Hadejia a matsayin mataimakin shugaban ma’aikata a ofishin mataimakin shugaban kasa.

By:

Posted in:


Leave a comment

Design a site like this with WordPress.com
Get started