An shiga zaman ɗar-ɗar a unguwannin Sheshe da Makwarari zuwa Kwanar Goda da ke birnin Kano.

Mai Rahoto. Huzaif Usman

Huzaif Usman. Reporter



Hakan dai ya biyo bayan kashe wani matashi mai suna Yusuf mazaunin unguwar Sheshe da wasu ɓatagari suka yi a Kwanar Goda.

Lamarin da ya janyo samun rikicin tsakanin unguwannin sai dai ƴan sanda sun kawo ɗauki inda suka kora matasan da suka yi yunƙurin neman ɗaukar fansa

Yanzu haka dai tuni unguwannin suka ɗaɗe inda aka rufe shaguna da gidaje.

Dama an ɗauki tsawon lokaci ana zaman doya da manja tsakanin ɓatagarin matasan da ke waɗannan unguwanni.

Kawo lokacin haɗa wannan rahoto hukumomin tsaro ba su ce komai ba a kai.

By:

Posted in:


Leave a comment

Design a site like this with WordPress.com
Get started